Thursday, May 31, 2007

Ya Ghiyathul Mustagithina; Daga Hayatu bin Sa'id

Hayatu bin Sa'id baya bukatar gabatarwa ga mutane, domin ga wanda yasan tarihin daular Fulani ta Sakkwato, yasan irin gwagwarmayar da aka sha da shi, da kuma yadda yayiwa Daular tawaye. Wanda, bayan hakan yayi mubayi'a ga Muhammad bin Abdullahi al Mahdi,na Sudan. Mahdi ya nada shi a matsayin halifansa a Daular Sakkwato, inda ya nemi Sarkin MUsulmi na wannan lokacin da yayi masa mubayi'a. Rashin samun nasarar hakan ce ta sanya ya koma ya hada kai da Rabih bin Salih (Rabeh). Inda daga baya suka samu sabani, ya dai rasu a wani karo da suka yi da Rabih. Ya rubuta wannan waka ce, a wani shagube da yayiwa yan'uwansa, a saboda irin mummunar fahimtar da suka yi masa.
Ga dai wakar;

1Ya Ghiyathul mustaghithina
2-na wa khairal nasirina
3Agaza ni kadda ka barni
4Ga dibarata ta kaini
5Yi dibara mai dibara
6Rahmanu ka jikaina
6Rabbu dubanni da rahma
7Anta khairil Rahimina
8Rahamakka sabiqata
9Jin kanka wabilina
10Babu mai yi sai da yin ka
11Wanga zance haka nan na
12Kai kayi ba taliki ba
13Taliki kau ajizina
14Rabbu kai ad dai Qadirun
16Jallah Sarki Qadirina
17Babu sarki daga Allah
18Shi fa Sarkin Gaskiyana
19Wanda yai sammai da kassai
20Wanda yayi dare da rana
21Wanda yai duniya da Barzakh
22Bata tsar mai ko ina na
23Wanda yai ran al-Qiyama
24Shi Azizi na gwanina
25Wanda yai wuta yayi al-Jan
26-na hakika Fatirina
27Agaza ni na kiraka
28Don Muhammadu yo i'ana
29Rabbu tsarshen daga kaidin
30Masu kaidi mufsidina
31Masu hasda da Adawa
32Da gamani kha'inina
33Sare kunci duk na makri
34Jallah Khairul makhirina
35Jallah kai ka tsadda Nuhu
36Shi da Hudu ga kafirina
37Jallah kai ka tsadda Ibra
38-him ga kaumun mu'tadina
39Kai fa kacce kana haqqun
40Fika nasarul muminina
41Don Muhammadu ya ilahil
42Arshi tsarshen makiyana
43Bani ikon shafe bid'a
44Bani ikon raya sunna
45Yo ijaba nai salati
46Ga Muhammadu dan Amina
47Hakaza Allai Sahabbai
48Duk jama'a tabi'ina

Sunday, May 13, 2007

Wakar Gyaran Kano; Daga Dr Aliyu Aqilu 1975

Wannan waka an rubuta ta ne a 1975, ya kuma yi tane domin wani hangen nesa da yaga Kantomman Kano na weannan lokaci yayi, wato Dr Uba Adamu. A hirar da nayi da Dr Uba Adamu, a gidansa cikin watan April, ya bayyana mini cewa " Cikin 1974 ne suka yi tunanin, kawo gyara a tsarin zamantakewar birnin Kano. A saboda haka suka kawo wani tsari, wanda hakan ya haifar da gina manyan tituna a Birnin Kano, da yin Kwalbatoci, da kuma wajejen zuba shara. A wannan lokacin ne akayi Manyan titunan da ake amfani dasu har yanzu a birnin Kano. Aka kuma yi musu Kwalbatoci a gefunansu, da kuma wajejen zuba shara". A saboda jin dadin wannan aiki ne, ya sanya Dr Aliyu Aqilu ya yi wannan waka. Ga dai wakar


Zan je ziyarar shugaba
Dattijo Kantoma Uba.

Bazan shiru na kawai ta ba
In ba da na ce Rabbu ba.

Sarki guda daya wahidi
Bazan takaita kiransa ba.

Bayan fadar Allah da gai da
Manzo Muhammadu Mujtaba.

Me zai biyo bayan su ne
Na abin nufi da yake gaba.

Haka ne akwai wani dan batu
Da ba zan ki tunkarar sa ba.

Ga dai bayani dan kadan
A takaice ba dungunsa ba.

Niyar ziyara ce dani
Zancenta yau zan bayyana.

Mai tambaya ya so yaji
Domin ya amfana gaba.

Manufar ziyarar wacce nai
Maganarta tun farko gaba.

Ya zuwa ina wai zani kai
Mai tambaya bai aibu ba.

Zan bayyana masa ne ya ji
Bazan yi kwauro gun sa ba.

Zan dau ziyara ne ni kai
Ta kano gari ba kauye ba.

Wajen masoyina abin
kamna sahihin Shugaba.

Shine Muhammadu Adamu
Kantoma mai lakabi Uba.

Dattijo din nan adali
Mai tausayin jama'a Uba.

Bangon tama ki faduwa
Sha kabra garnakaki Uba.

Matsayinka din nan kai can
Canta da shi malam Uba.

Illimi zalaka ke gare
ka da kwarjini na kwarai Uba.

Ga hattara ga hankali
Kantoma ga hangen gaba.

Illimin makamar zamani
Da sanin sharia tun gaba.

Ka san su ka kuma dandake
Ba yau kawai ka tsire suba.

Birnin Kano da wajenta duk
Ta samu babban cigaba.

A wajen nizafa in ka du
Ba kauyuka ba a bar suba.

Balle cikin birnin fa
Ba wai bane ba inke ba.

Kwatami cakal yau babu shi
Shara butsa bamu ganta ba.

Sarari a hanya ya dadu
Albarkacin himmar Uba.

Duk tarkace an kauda su
Daga ko ina ba a bar shi ba.

Sababi da wane mun ka sami
wannan gimgimemen cigaba.

Mun samu kakkaifan mutum
Mai kokari ba kasa ba.

Gwarzon maza namijin tsaye
Inuwa ba a bisne ki ba.

Kantoma Muhammadu Adamu
Dattijo mai lakabi Uba.

Bompai da Rimin Dada sun
Maka godiya malam Uba.

Sabon gari da Tudun wada
Sun gode mai daraja Uba.

Tarauni su da Giginyu sun
Yi yabo ga mai daraja Uba.

Gandu Sharada da Dorayi
Da Salanta., Calawa gaba.

Jama’ar da ke Fanshekara
Duk sun yi san barka Uba.

Waika da Jajira, Gobira
Wa, sun yi godiya malam Uba.

Kurna, Fagged da Gwagwarwa
sun maka godiya malam Uba.

Na sauka Fanisau mutan
Gama sun game da yabon Uba.

Ungogo, Kunya suna fadar
Madalla-madalla Uba.

Wannan Sadauki adali
Dattijo bai yashe mu ba.

Kub! Dai yawa kuwa lara bugu
Daya ta mace bata tashi ba.

Ya watsa rundunar
Sauro a yau bamu ji shi ba.

Bana nufin guda da dai
Ban daura niyyar yinta ba.

Amma dalili ya saka, ni
Na yi ta ban shiryeta ba.

Domin saboda farin ciki
Dadin zamanmu da kai Uba.

Zai sa ni Kwalla yar kadan
Watakil bakwa zarge niba.

Sirri na kokon zuciya
Fuska bata rasa jin sa ba.

Yururui! A yau na randama
Kodai da ban sabeta.

Amma akwai Magana daban
Da ba zan iya ban yi taba.

Domin ta nai mini kaikayi
Na zo ka sosa wajen Uba.

Najasa da ke yi barkatai
Haka nan butsa! An zuzzuba.

Ba kariya ko yar kadan
Daga baya har ya zuwa gaba.

Ka ga sangamemen saurayi
Bama su yara kanana ba.

Ya yaye al’aura a fi
Li bada jin kunyarsa ba.

Wannan abin bisa gaskiya
Ban samu jin dadinsa ba.

Domin akwai ill agama
Baki ba za su yabe mu ba

Harma sukan zarge mu ne
Ba wai bane, ba inke ba.

Ni naji sanda suke fade
Kuma na gwada na jarraba.

Kasan ni kan fita ne waje
Zancenga ban kage shi ba.

Wannan ta ja mini damuwa
Na tafo ka maganta Uba.

Ai ya kamata ka tsawata
Kuma kar a kara nan gaba.

Nasan ka baka rurumi
Kuma baka lalaci Uba.

Me maida kai kake mai kula
Ga abinda duk ka saka gaba.

Tsuguna da tashi ba’a yin ta
A ofishin malam Uba.

Baka shiri da munafuki
Cece-kuce baka ji shi ba.

Kowa shigo da maganganu
Mara sa shiri a gaban Uba.

Kudarsa zai kuwa dandana
Dadin karon bai ji shi ba.

Su kwaramniya da rigingimu
Da hayaniya an zuzzuba.

Duk dai a karata dole ne
Ayi gaskiya a gaban Uba.

Domin kurum shi kayi shi ji
Kowa abinda ya rattaba.

Suna daban yau zan fada
A gareka yau malam Uba.

Kere kana fasa kan maki
Bin gaskiya baka san shi ba.

In kun tuna nace da ku
Guda bana rika yin ta ba.

Amma fa har haka dan ku ji
Dadi bazai inganta ba.

In banda an ware shi an
Yafa shi an more shi ba.

Kash! Nan wajen zan dakata
In sa alama sai gaba.

Ni ne Aqilu Aliyu na
Gaisheka mai daraja Uba.

Kantoma huta lafiya
Sai lokaci wani nan gaba.

In Rabbana ya kaddara
Mana saduwa ban mata ba.

Bana yawaita maganganu
Sai addu’a zan kattaba.

Ya Rabbi ya Sarki Gwani
Allah ka ja zamanin Uba.

Amin saboda abin biya
Da yabo Muhammadu Mujtaba.

Tamat bi AunilLahi mun
Bidi taimako nasa tun gaba.>

Saturday, May 12, 2007

Wakar da ake Sanin Halin mata da ita; Muhammad Dangani Katsina

Wannan waka dai ta shahara a kafafen watsa labarai na Kano da Kaduna,domin akan watsa ta a shirye-shirye da dama.Ga dai wakar.

Bismillahir Rahmanir Rahim
Wasallallahu ala Nabiyul Karim

To bismiLlah Allah Sarki
Mai abu mai komai mai kyauta

Bani zalaka, bani fasaha
Inyi bayani na, a fahimta

Zanyi bayani halin mata
Zani rubuta, don a karanta

Kasan mata sun kasu ukku
Zo kusa in na fada ka rubuta

Akwai mata mai tsoron Allah
Bata nufin kowa da mugunta

Akwai wata ga barna ga gyara
Gata da saukin kai ga cuta

Sai ta ukunsu gadangama kenan
Bata nufin gyara sai cuta

Bata nufin hairi ga mijinta
Baga kiyoshi,ba ga makwabta

Bata nufin gyara sai barna
Sai duk safe ta cuci mijinta

Ya tafi office kokuma kanti
Bata kara zama dakinta

In mai noma ne ko zage
Ya tafi gona, zaure za ta

Tana nema taga masu wucewa
Wai ita dai suga kyan fuskarta

In taga sunki shiga harkarta
Sai kaji tace zata makwabta

Kaji irin halayen mata
Munana,manyan, makwadaita

In mace bata da kunya barta
Kama da miya,in ba gishirinta

In mace bata raga maka barta
Daina nufinta kabar sha'awarta

In mace ta zama bata ragama
Ko ka sota, kana kuma kinta

In mace, shashanci ya gameta
Ba mai kara ganin kirkinta

Bata nufin Allah da Ma'aiki
Sai bidi'a ita ke ka gunta

Taji ana Biko tai mika
Sai kaji tace Biko zata

Ba dangin iya babu na Baba
Ko kace ta bari, can zata

Wannan mace,ba mace ce ba
Dai na nufinta kabar sha'awarta

Natsuwa itace mace,ko yar wace
In kaga ba natsuwa,ka bajeta

Kasan mata sun iya karya
Sun iya yadda suke shirgata

Ba duk mace ke son addini ba
Nufinsu a basu kudi, su bukata

Matar da ta zam bata san Allah ba
Ba ta kara zama dakinta

Sai ta fito a tashar Takatale
Sai tai batsa gaban kanwarta

In kace mata, wance ki lura
Baka hana ni bugun cinyata

Babu ruwanta da kunya faufau
Ga Ashar, ko ciwake yana kunyarta

Sanarwata itace ga mazaje
Kar a yawaita kwadai, a takaita

Aure ba abu ne ba na wasa
Bar neman kyau, nemi nagarta

Ni nasan mace, komi kyaunta
Indai babu hali da nagarta

Kana sha'awarta, kana kuma sonta
Badan Allah ba kana kyale ta

Don haka, tun farko ka tsaya tsaf!
Kai nazari da irin halinta

In mace ta zama, shagiri girbau
Ko ka aureta, baka iyata.

Kun ji mazaje, kar ku kiya man
Ku lura da duk farkon maganata

Akwai mata na nan su shidda
Zo kusa inna fada ka jimilta

Akwai dibgau! Mai dibge mijinta
Ba ta jira ga fada shi taya ta

Danbago, mai zurfin tumbi
Ba ta takowa sai ta cikinta

Sai shirwa ita dai tayi fige
Kan ta shigo daki sai ta sata

Ratata, sarkin magana ce
Tun daga nesa, kana jin kanta

In maganar mace tayi yawa, kaji
Tun daga nesa, kana jin kanta

Wannan mata, tayi hasara
Sai a nada mata sarki wauta

Sai Malali, ita dai tayi kwance
Ta ki ta tashi, ta nemi na kanta

Ba ta kadi, kuma bata sanaá
Sai na mijinta, ya bata, ta sata

Sai ta cikon shida, mai mulkin kai
Ba mai sa ta, bare shi hana ta

Aure ne, ni nis sa kaina
In ka matsa mani, in tafiyata

To shida ta cika ban kara ba
Akwai saura, amma na takaita

Akwai saura, amma na kaita
Ka shaida akwai mata masu kazanta

In mace ta zam bata da tsafta
wannan kam, ta cuci mijinta

Yin tsafta, ta jiki da tufafi
Shine ke hana yadon cuta

Wadda ta zam, bata wanke tufa ba
Shike shaida, anga kazanta

Zani tuna muku in kun manta
Kashedi, da mata masu kazanta

Sun gaza wanke tufa da tukwane
Sun ki kula da abinci su kyauta

Ta gaza share cikin dakinta
Balle na mijinta, bale fuskatta

Kun ji isharata ku kiyaye
Ku lura da duk farkon maganata

Akwai barna ga mazaje
Zamu fada musu, don su raga ta

Wadansu maza dauka da ajewa
Sun dauko mace, sai su aje ta

Ba laifin tsaye, babu na zaune
Sai kaga basu zuwa dakinta

Ran aikinta ba zai fara'a ba
Ko magana tai, bashi kulawa

Duk namijin da ya dau kwanan wata
In ya hana mata, don bai son ta

Yaki bsatun Allah da maáiki
ya kashe kansa, saboda mugunta

Mata gunku amanar Allah ce
Don Allah maza ku rike ta

In mace tai maka laifi daure
Sai ka tuna, ai kai ka aje ta

Su mata halinsu mugunta
Sai dai-dai ke, basu da keta

Macce, mijinta ko sarki ne
bata yaba masa, sai in bata

Macce mijinta ko malam ne
Bata yabonsa tace da nagarta

Tana iya cewa miji mataulaci
Koda yayi kudin Dantata

Su ka bugu su riga kai kara
Ba ai magana ba su je su tsirata

In mace ta shirya maka karya
Ko boka kam, bashi iyata

Macce tana shiryawa mijinta
Karya, don ya bari tayi cuta

Tâce mashi zata gidan kanwarta
Ko kuma zata ta gaida uwaye

Ta fita, ta samu ta sulale
Ta shiga yawo santa-santa

Ba ta gidan iya, bata na Baba
Kaji nufinta ta sheke ayarta

Don haka mata, ba'a iya musu
In kaji sun magana ka aje ta

Kowace mata na da halinta
Wadansu da kyau, wasu ko da mugunta

Wata in suka fara fada da mijinta
Sai ta rike shi, tace ya kasheta

In kuma yaki ta kama tufarsa
Ace ta sake shi, tace ya kasheta

Ko kuma yanzu ka bani takarda
In kuma ka ban in ketata

In kuma kace anshi takardar
Sai kaji tace, bani riketa

Ita dai sababi ta ka so ta aza mai
Indai yace bashi sakinta

In ka hada ta da Allah sannan
Tafi matsa maka don tsiwarta

Kai kuma gaka kana jin kunya
Ga shari'a ka zage ka kasheta

Don haka sai kowa yayi sannu
Ya nemi hali mai kyau da nagarta

Ba'a sayan mota don kyanta
Sai kaya, da gudu, da nagarta

To haka ne mace, komi kyaunta.
Indai babu hali da nagarta

Kamar mota take komi kyaunta
Indai ba tafiya, bari sonta

Kyan ladabin mace tai wa mijinta
In taki ya mishi, ta kashe kanta

Kui ladabi mata ku kiyaye
aure ba'a gama shi da bauta

In mace tai ladabi ta kiyaye
Allah sarki, shi ka biyanta

Ku mata ku jiya, ku kiyaye
In kuma kun ki, kui mahukunta

Ran mutuwa, da gamo, da kasawa
Sai a tuna maka, in ka mance

In mace tabi mijinta da gaske
Tayi hakuri ta tsaya dakinta

Bata ganin wani banda mijinta
Allah zai mata, babbar kyauta

Miji babban abune bi mjinki
Dai na ganin waccan da mijinta

Bishi, ki so shi, ki bar raina shi
Ko shine sarkin matalauta

Don ki sani Allah ya aza mai
Shi aza masi, shi zai kyauta

Shi abu duk aikin Allah ne
Allah shike bada wadata

Ya kasa bayi fanni-fanni
Shi yai ma'azurta, yai matalauta

In niyyarki gudun matalauta
Sai ya so sannan ki wadata

Shi Allah ba ai masa wayo
Yanda yaso, haka za shi hukunta

Ki hakuri ki tsaya ga mijinki
In ya wadatu, sai ki wadata

Ya Allahu muna rokonka,
ya Allah ka bamu wadata

Ka bamu abinci ckin suturarmú
Allah kadda ka nufe mu da sata

Duk makiyanmu aza mu akansu
Duk sharrin da su kai da mugunta

Ka daukaka addini bisa komai
Ya Allahu bidia ka kashe ta

Kai tsira ga Muhammadu Ahmadu
Don dakin makka, don siffatai

Sahabi nabiyu, da ahlil baiti
Ahlil abaí kaza makusanta